Connect with us

News

WAEC Ta Sanar Da Sabon Tsarin Gyara Jarrabawar Da Mutum Ya Fadi Ba Sai Ya Yi Jiran Shekara Daya Ba

Published

on

WAEC Ta Sanar Da Sabon Tsarin Gyara Jarrabawar Da Mutum Ya Fadi Ba Sai Ya Yi Jiran Shekara Daya Ba

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Hukumar WAEC ta sanar da cewa daga yanzu waɗanda suka faɗi wani darasi na jarrabawarsu za su iya sake rubuta shi ba sai sun jira tsawon shekara ɗaya ba.

Advertisement

Shugaban sashen hulɗa da jama’a na hukumar John Kapi ne ya bayyana haka a yayin tattaunawa a kan shirin AM Show na JoyNews a Ghana.

An Samu Bullar Sabuwar Cuta Mai Makamanciyar Covid-19 A Asibitocin Kasar China

Wannan sabon shiri zai bai wa ɗalibai damar sake rubuta jarabawarsu ta Babbar Sakandare ta Afirka ta Yamma (WASSCE) a farkon watan Janairu da Fabrairu 2025.

Advertisement

Wannan babban canji ne idan aka kwatanta da shekarun baya, inda ɗalibai ke jira har sai sawon shekara ɗaya

“Ɗalibai da suka ga sakamakonsu yanzu kuma suka gano suna buƙatar sake rubuta takarda ɗaya ko biyu suna da har zuwa 8 ga Janairu don yin rijista ta yanar gizo ta shafinmu ko a cibiyoyin intanet da WAEC ta amince da su.

Advertisement

“Za a gudanar da jarabawoyin daga ranar 24 ga Janairu zuwa 15 ga Fabrairu 2025,” in ji Kapi

 

Advertisement

 

DAILY POST

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending