Connect with us

News

Ranar Litinin Mai Zuwa Za’a Fara Rubuta Jarabawar WAEC

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Hukumar shirya jarabawar kammala makarantun sakandire ta yammacin Afrika, WAEC, Ta ce za’a fara rubuta jarabawar kammala kammala makarantun sakandire ta SSCE daga ranar Litinin mai zuwa 8 ga watan da muke ciki zuwa ranar 23 ga watan Yunin bana a Najeriya.

 

Advertisement

Da yake yiwa manema Labarai karin haske, Shugaban Ofishin hukumar a nan Najeriya, Patrick Areghan, Ya baiyana cewar mutane Milyan 1 da dubu 621 da 853 daga makarantun sakandire dubu 20 da 851 zasu rubuta jarabawar a bana.

Kotu a Birtaniya za ta yanke wa Ekweremadu da matarsa hukunci a yau

Ya kuma kara da cewar Daliban zasu rubuta jarabawar ne akan darussa daban daban har 76, A yayin da kwararrun manyan malaman makarantun sakandire dubu 30, zasu yi aikin saka ido a lokacin rubuta jarabawar ta SSCE.

Advertisement

 

Daga nan sai ya gargadi makarantu da su guji kin dora makin jarabawar gwaji ta daliban da zasu rubuta jarabawar akan lokacin da aka tsara.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending