News
Daliban Jami’ar Northwest Sun Kai Gudummawa Gidan Gyaran Hali A Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
A wani yunkuri na tallafawa al’umma, wasu daliban da suka kammala karatun su a fannin Ilimin Kimiyyar Bayanai da Dakin Adana Bayanai (Library and Information Science) a Jami’ar Northwest, Kano, sun kai gudummawar kayan bukatun yau da kullum zuwa Gidan Gyaran Hali da Tarbiyya na Kurmawa, Kano.
Ziyarar ta gudana ne karkashin jagorancin Kwamared Abdurrashid B. Imam, tare da wasu daga cikin abokan karatu, inda suka bayyana cewa manufar wannan aiki shi ne tallafawa wadanda ke tsare a gidan gyaran hali, tare da tunatar da al’umma muhimmancin taimakon marasa galihu.
Majalisar Dattijai Ta Naɗa Sanata Babangida Hussaini a Matsayin Ciyaman na Kwamitin NWDC
A cewar B. Imam, “Mun sake lekawa gidan gyaran halin ne domin kara bada gudummawar mu ga waɗanda suke rayuwa a wancan gida.”
Har ila yau, ya yi kira ga daidaikun al’umma, kungiyoyin dalibai, da kungiyoyin da ba na gwamnati ba da su ci gaba da tallafawa waɗanda ke killace a gidajen gyaran hali domin ba su damar inganta rayuwarsu.
A karshe, shugaban tawagar ya mika godiya ga dukkan wadanda suka bada gudummawa, wanda hakan ya ba su damar aiwatar da wannan aikin alkhairi.
-
News21 hours ago
Jam’iyyar Labour Party Ta Yi Alkawarin Kafa Hukumar Kula Da Hayar Gidaje A Kano
-
News3 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News6 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
