News
Shugaba Tinubu Ya Tafi Faransa
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya tafi Faransa gabanin taron ƙasashen Afrika
Tinubu zai shafe mako guda a Faransa, inda daga nan zai wuce taron ƙungiyar ƙasashen Afrika AU, da zai gudana tsakanin 12 zuwa 16 ga watan Fabrairu a birnin Addis Ababa na Habasha.
Mai Ba Shugaban Kasa Shawara na Musamman kan Bayani da Tsara Dab’i, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa a ranar Laraba.
Ya ce tafiyar Shugaban Kasa zuwa kasar Turai na da dalilai na kashin kansa, tare da bayyana cewa ziyarar ta kasance ne a hanyarsa zuwa Addis Ababa, babbar birnin Habasha.
Mai magana da yawun shugaban kasa ya bayyana cewa Tinubu zai isa Addis Ababa farkon mako mai zuwa don taron koli na Kungiyar Tarayya.
Details soon
-
News2 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News7 days ago
2027: INEC Ta Tabbatar Da Ibrahim Ali Amin Little A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano A Jam’iyyar ADC
-
News5 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
