Connect with us

News

Ana Fargabar Masu Kwacen Babur Sun Hallaka Wani Mutum A  Unguwar Kwachiri A Kano

Published

on

Dole Kowacce Gawa Ta Biya HarajiGwamnati

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Rahotanni daga jihar Kano sun tabbatar da cewa wani mutum da ke sana’ar achaba ya rasa ransa sakamakon harin da wasu da ake zargin barayin babur ne suka kai masa a daren Laraba.

Shaidu sun bayyana cewa lamarin ya faru ne a bakin titin da ke tsakanin Airport da unguwar Kwachiri, inda ɓata garin suka farmaki mutumin, suka yi masa rauni mai tsanani ta hanyar yanka shi, sannan suka tsere da babur ɗinsa.

AZUMI: Gara A Taimaka A Rage Farashin Abinci Fiye Da Ware Biliyoyi Don Rabo —Yasir Sani 

Wannan lamari ya haifar da fargaba a tsakanin masu sana’ar achaba da ma al’ummar yankin, inda ake kira ga hukumomi da su dauki matakin da ya dace domin tabbatar da tsaro a wannan wuri da kuma dakile ayyukan masu aikata irin wannan danyen aiki.

Hukumomi dai ba su fitar da wata sanarwa kan lamarin ba a yanzu, amma ana sa ran za a gudanar da bincike domin gano gaskiyar al’amarin da kuma daukar matakin da ya dace.

 

Advertisement

 

EXPRESS RADIO 

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending