Connect with us

News

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari A Kauyuka Biyar A Kaduna

Published

on

 

Yan bindiga sun yi wa wasu kauyuka biyar a karamar hukumar Kachia ta Jihar Kaduna dirar mikiya, inda suka tilasta wa mazauna tserewa tare da kona wata mota da babur guda.

Kauyukan da harin ya shafa sun hada da Unguwan Tauka, Unguwan Lalle, Sannu da Zuwa, Tsauni Dodo da Dandauka. Baya ga haka, ‘yan bindigar sun kai farmaki a wani yankin Fulani da ke Kubuwo, inda suka sace wasu matasa makiyaya guda uku.

Gobara Ta Lakume Rayuka 7, Ta Haddasa Asarar Naira Miliyan 50 A Kano

Wani shugaban yankin ya bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe shida na yamma bayan da ‘yan bindigar suka tsere daga farmakin da sojoji suka kai a dajin Kurutu-Azara. Rundunar ‘yan sandan yankin ta tabbatar da aukuwar harin amma bata bayyana yawan asarar rayuka ko jikkata ba.

 

 

Advertisement

PRNIGERIAN

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending