News
Tinubu ya gana da gwamnan Ebonyi, Umahi
Daga yasir sani Abdullahi
Jagoran Jami’yar APC na ƙasa a ranar Juma’a ya gana da gwamna David Umahi na jihar Ebonyi.
In za a iya tuna cewa, wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta kori Umahi tare da mataimakinsa a ranar Laraba saboda sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Sai dai Umahi ya daukaka kara kan hukuncin.
An jiyo cewa dan takaitaccen ganawar da gwamnan ya yi da Tinubu wanda ya gudana a Abuja ranar Juma’a bazai rasa nasaba da hukuncin kotu ba da kuma rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar APC.
Tinubu da Umahi dai sun nuna matukar sha’awarsu ta neman tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC mai mulki a 2023.
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News5 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
