Connect with us

News

Tinubu ya gana da gwamnan Ebonyi, Umahi

Published

on

Daga yasir sani Abdullahi

 

Advertisement

 

Jagoran Jami’yar APC na ƙasa a ranar Juma’a ya gana da gwamna David Umahi na jihar Ebonyi.

Advertisement

In za a iya tuna cewa, wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta kori Umahi tare da mataimakinsa a ranar Laraba saboda sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.

Sai dai Umahi ya daukaka kara kan hukuncin.

Advertisement

An jiyo cewa dan takaitaccen ganawar da gwamnan ya yi da Tinubu wanda ya gudana a Abuja ranar Juma’a bazai rasa nasaba da hukuncin kotu ba da kuma rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar APC.

Tinubu da Umahi dai sun nuna matukar sha’awarsu ta neman tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC mai mulki a 2023.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending