News
Kotun Ta Yanke Wa Wani Magidanci Mai Shekaru 56 Hukuncin Daurin Rai-Da-Rai
Babbar Kotun Jihar Ekiti da ke zamanta a Ado-Ekiti, ta yanke wa wani magidanci mai shekaru 56 hukuncin daurin rai-da-rai bisa samunsa da laifin yi wa agolarsa mai shekaru 14 fyaɗe.
Kotun ta yanke wannan hukunci ne bayan gurfanar da wanda ake tuhuma a gabanta a watan Oktoban shekarar 2024, inda aka bayyana cewa laifin ya faru a cikin gida, watanni bakwai da suka gabata.
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari A Grow Homes Estate, Sun Yi Garkuwa Da Mutane Biyu
Mai gabatar da ƙara, Julius Ajibare, ya gabatar da shaidu guda shida da suka tabbatar da cewa wanda ake tuhuma — mijin mahaifiyar yarinyar — ya aikata laifin fyade.
Haka kuma, an gabatar da sakamakon binciken likita da wasu ƙarin hujjoji da suka tabbatar da sahihancin zargin da ake masa.
Ko da yake lauyan wanda ake tuhuma, Olajide Adedeji, ya gabatar da shaida guda ɗaya domin kare wanda yake wakilta, kotun ta yanke hukuncin daurin rai-da-rai bayan ta gamsu da shaidu da hujjojin da aka gabatar mata.
Hukuncin ya jaddada kudirin kotuna wajen yaki da aikata fyaɗe musamman ga ƙananan yara, da kuma tabbatar da kariya ga marasa galihu cikin al’umma.
