Connect with us

News

Ana Zargin ‘Yan Bindiga Sun Sace Budurwa Sa’o’i Kadan Kafin Daurin Aurenta A Sokoto

Published

on

IMG 4719 (1)

Wasu ’yan bindiga sun kai farmaki a kauyen Chacho da ke ƙaramar hukumar Wurno a jihar Sokoto, inda suka yi garkuwa da amarya,kwaayenta da wasu daga cikin mahallara taron.

Lamarin ya faru ne daren Asabar bayan da maharan suka shiga kauyen kusan ƙarfe Daya na dare, suka soma harbe-harbe kafin su kwashe mutane.

Advertisement

Dakarun Soji Sun Ceto Mutane 7 Da Aka Sace A Kano

Rahotanni daga yankin sun ce mata da dama da suka taru domin taimakawa amaryar wajen shirye-shiryen bikinta suma an sace su.

Shugaban jam’iyyar APC na jihar, Isah Sadeeq Achida, ya tabbatar da afkuwar lamarin, sai dai ya ce ba zai tabbatar ko amaryar na cikin wadanda aka sace ba, saboda ba a tantance adadin mutanen da aka dauke ba tukuna.

Advertisement

Daily Post ta yi ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Ahmed Rufai, amma bai amsa kiran waya ba

Harin ya faru ne awanni kaɗan bayan da aka ce an biya kudin fansa na Naira miliyan huɗu da babur guda domin sako wasu da aka sace a garin Rabah.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending