News
Ana Zargin ‘Yan Bindiga Sun Sace Budurwa Sa’o’i Kadan Kafin Daurin Aurenta A Sokoto
Wasu ’yan bindiga sun kai farmaki a kauyen Chacho da ke ƙaramar hukumar Wurno a jihar Sokoto, inda suka yi garkuwa da amarya,kwaayenta da wasu daga cikin mahallara taron.
Lamarin ya faru ne daren Asabar bayan da maharan suka shiga kauyen kusan ƙarfe Daya na dare, suka soma harbe-harbe kafin su kwashe mutane.
Rahotanni daga yankin sun ce mata da dama da suka taru domin taimakawa amaryar wajen shirye-shiryen bikinta suma an sace su.
Shugaban jam’iyyar APC na jihar, Isah Sadeeq Achida, ya tabbatar da afkuwar lamarin, sai dai ya ce ba zai tabbatar ko amaryar na cikin wadanda aka sace ba, saboda ba a tantance adadin mutanen da aka dauke ba tukuna.
Daily Post ta yi ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Ahmed Rufai, amma bai amsa kiran waya ba
Harin ya faru ne awanni kaɗan bayan da aka ce an biya kudin fansa na Naira miliyan huɗu da babur guda domin sako wasu da aka sace a garin Rabah.
-
News6 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
-
News1 day ago
Ana Zargin Matar Aure Da Shaƙe ’Yar Kishiyarta Mai Shekara 3 Har Lahira
-
News13 hours ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
