News
Gwamnan Jihar Osun Adeleke Ya Sauya Sheƙa Zuwa Jam’iyyar Accord
Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya sanar da sauya sheƙa zuwa jam’iyyar Accord, kwanaki kaɗan bayan ya fice daga jam’iyyar PDP.
Adeleke ya bayyana komawarsa Accord ne cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X da yammacin ranar Talata.
Kano 2027 : Kamar A Hankali A Hankali Shugabancin Jam’iyya Na Karkata Ga Sanata Barau
A cikin sakon nasa, gwamnan ya ce: “A yau mun gabatar da jam’iyyar Accord a matsayin sabon dandali ga jama’ar Osun. Daga Osun West zuwa Osun East har zuwa Osun Central, wannan ita ce jam’iyyarmu, sabon matakinmu zuwa ga nasara a watan Agusta na shekara mai zuwa.”
Advertisements
