News
KANO: Ba A Samu Asarar Rai Ba A Gobarar Da Ta Tashi A Babban Asibitin Rogo
Shugaban Karamar Hukumar Rogo, Alhaji Abubakar Mustapha Rogo, ya ce babu wanda ya rasa ransa a gobarar da ta tashi a wani bangare na Babban Asibitin Rogo da ke jihar Kano.
A cewar sa, gobarar ta haifar da ɗan razana ga marasa lafiya da ma’aikatan jinya, kafin jami’an kashe gobara da mazauna yankin su shawo kan ta.
Jami’in Yaɗa Labarai na Karamar Hukumar, Abdu Bako Abdullahi (ANIPR), ya ruwaito cewa lamarin ya haddasa asarar dukiyoyi masu daraja, inda ya yi kira ga Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, da ya duba halin da al’umma suka shiga.
Ya ce sake fasalin asibitin zai taimaka wajen farfaɗo da hidimar kiwon lafiya a yankin, musamman ma matakin farko.
Alhaji Abubakar ya kuma yaba wa jami’an tsaro da Hukumar Kashe Gobara kan yadda suka tashi tsaye wajen dakile wutar cikin gaggawa.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
