News
Ibrahim Little Zai Garzaya Kotu Kan Yunkurin Ganduje Na Kafa Hisba Mai Zaman Kanta A Kano
Tsohon ɗan takarar gwamnan Kano, Ibrahim Ali Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke yi ƙarƙashin jagorancin tsohon gwamna, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, na kafa wata Hisbah mai zaman kanta a jihar.
Little ya ce wannan yunƙuri barazana ne ga zaman lafiyar jihar, tare da iya haifar da rikice-rikice da rashin daidaito a tsarin tsaron al’umma.
Mataimakin Gwamnan Bayelsa Ya Rasu Sa’o’i Bayan Ya Yanki Jiki Ya Faɗi A Ofishinsa
Ya bayyana cewa ya umarci lauyoyinsa su aika wa masu wannan yunƙurin takardar gargadi, ya na shawartar su da su janye wannan tafiya nan take.
A cewarsa, idan suka ƙi bin umarnin, zai garzaya kotu domin dakatar da duk wani yunƙuri da zai iya haifar da rikici ko tarnaƙi ga tsarin doka a jihar
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
