News
Mataimakin Gwamnan Bayelsa Ya Rasu Sa’o’i Bayan Ya Yanki Jiki Ya Faɗi A Ofishinsa
Mataimakin gwamnan jihar Bayelsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo ya rasu a yau Alhamis.
Da misalin ƙarfe 1:30 na rana aka ruwaito cewa ya yanki jiki ya faɗi a ofishinsa, inda aka gaggauta garzayawa da shi zuwa Babban Asibitin Tarayya da ke Birnin Yenagoa, sannan aka tabbatar da rasuwarsa jim-kaɗan bayan haka.
Jami’an NAFDAC Sun Kona Jabun Kayayyaki Na Naira Biliyan 5 A Nasarawa
A ranar 5 ga watan Satumban shekarar 1965 aka haifi marigayin, kamar yadda majiyoyi suka shaida.
Majiyoyi daga gidan gwamnatin jihar sun bayyana shi a matsayin mai ƙoƙarin kiyaye aikinsa bisa sadaukarwa da jajircewa.
A cewar ShaharaReporters, Mataimakin gwamnan ya shiga mawuyacin hali ne a lokacin da aka kai shi sashen gaggawa na asibitin.
Wani ɗan gidansu da ya gana da manema labarai ya tabbatar mutuwar jim-kaɗan da kai shi asibitin.
