Connect with us

News

Kotu Ta Aike Da Tsohon Ministan Kwadago Chris Ngige Gidan Yari

Published

on

FB IMG 1765538284676

Wata babbar kotun tarayya da ke Gwarimpa, Abuja, ta bayar da umarnin a tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige, a gidan yarin Kuje, bayan gurfanar da shi a gaban kotu bisa tuhuma takwas da suka shafi cin hanci da rashawa.

Advertisements
Advertisements

Hukumar EFCC ce ta gurfanar da tsohon ministan a gaban mai shari’a Mariam Hassan, inda ake zarginsa da aikata laifuka a lokacin da yake rike da mukamin ministan ƙwadago a gwamnatin tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari. EFCC ta bayyana cewa Ngige ya yi amfani da matsayinsa wajen bai wa abokansa kwangiloli ba bisa ƙa’ida a lokacin da yake kula da NSITF daga Satumba 2015 zuwa Mayu 2023.

Advertisements

Ngige ya musanta dukkan zarge-zargen da ake masa a zaman kotun. Mai shari’a Mariam ta dage ci gaban shari’ar zuwa ranar Litinin domin sauraron bukatar neman belinsa, tare da bayar da umarnin a ci gaba da tsare shi a gidan yarin Kuje har sai an kammala sauraron buƙatar.

Advertisements
Advertisements
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending