Connect with us

News

Dakarun Soji Sun Hallaka Ƴan Ta’adda 21 A Borno

Published

on

‎Burkina Faso ta saki sojojin Najeriya Da Take Rike Da Su Na Tsawon Kwanaki 10

Dakarun Rundunar Sojin Najeriya a ƙarƙashin Operation Hadin Kai sun kashe fiye da Ƴan ta’adda 21 a wani mummunan artabu da ya auku a ƙauyukan Sojir da Kayamla da ke kan hanyar Damboa–Maiduguri a Jihar Borno.

An gudanar da wannan farmaki ne tare da haɗin gwiwar Civilian Joint Task Force (CJTF).

Advertisement

MAAUN Ta Ba Dalibai 43 Masu First Class Guraben Karatun A Ƙasashen Waje

Wata majiya mai tushe a Hedikwatar Sojoji ta shaida wa Hukumar Labarai ta Najeriya (NAN) a Abuja a ranar Lahadi cewa artabun ya auku ne da misalin ƙarfe 12:15 na dare sakamakon sahihin bayanan leƙen asiri da suka nuna taron manyan ’yan ta’adda a yankin, waɗanda ake zargin suna shirin kai hare-haren haɗin gwiwa.

Majiyar ta ce dakarun sun gaggauta shiryawa tare da yin arangama da ’yan ta’addan—kimanin 100—da misalin tsakar rana a ranar Asabar.

Advertisement

A cewarsa, duk da yunƙurin wata ƙungiya ta ƙarin ’yan ta’adda ta kewaye dakarun, sojojin sun tsaya tsayin daka tare da amfani da ƙarfin wuta mafi rinjaye.

“An tabbatar da gawarwaki 17 a wajen, yayin da ake zargin wasu ƙarin sun jikkata ko suka mutu, ganin yadda aka ga sawun jini zuwa cikin dazuka na kusa.

Advertisement

“An kwace makamai, harsasai da sauran kayayyakin tallafi, yayin da dakarun ke ci gaba da matsa lamba don hana ’yan ta’addan samun ’yancin motsi.

“An yi janyewar dabara domin daidaita yanayi da bai wa dakarun damar sake tattaruwa, kuma an ruwaito cewa ƙwarin gwiwar sojoji na nan daram duk da tsananin artabun,” in ji shi.

Advertisement

Majiyar ta jaddada ƙudurin sojoji na ci gaba da kai hare-haren kai tsaye domin kare Maiduguri, Damboa da al’ummomin da ke kewaye a yankin Arewa maso Gabas.

 

Advertisement

 

PREMIUM TIMES

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending