News
Jami’an Yan Sanda Sun Kama Mutane 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Kano
Rundunar ’yan sanda ta Jihar Kano ta tabbatar da kama mutane biyar da ake zargi da hannu a ayyukan garkuwa da mutane da satar shanu, bayan gudanar da wasu ayyukan bincike na musamman bisa sahihan bayanan leƙen asiri a sassa daban-daban na jihar.
A cewar rundunar, kamen ya biyo bayan ƙoƙarin da ake ci gaba da yi na daƙile ayyukan masu aikata laifuka da ke barazana ga tsaro da zaman lafiyar al’umma. Jami’an tsaro sun bayyana cewa an samu nasarar ne ta hanyar haɗin gwiwa tsakanin ’yan sanda da mazauna yankunan da abin ya shafa.
Rundunar ta ƙara da cewa ana ci gaba da bincike kan waɗanda aka kama, tare da shirin gurfanar da su a gaban kotu da zarar an kammala binciken. Haka kuma, ta yi kira ga jama’a da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro haɗin kai ta hanyar kai rahoton duk wani abu da ke nuna alamun aikata laifi, domin tabbatar da dorewar tsaro a Jihar Kano.
-
News2 days ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
-
News2 days ago
Ana Zargin Matar Aure Da Shaƙe ’Yar Kishiyarta Mai Shekara 3 Har Lahira
-
News7 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
