News
Anthony Joshsua Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Hatsarin Mota
Shahararren dan damben boksin na duniya, Anthony Joshua, ya tsallake rijiya da baya a wani mummunan hatsarin mota a ranar Litinin.
Mutum biyu sun rasu a bayan motar da Anthony Joshua yake ciki ta yi gaba-da-gaba da wata babbar mota da ke ajiye a gefen titin, a yankin Makun da ke Jihar Ogun.
Siyasar Kano: Shin Kwankwaso Ne Zai Tura Gwamna Abba Jam’iyyar APC ko Kuwa Gaban Kansa Yake Son Yi?
Wakilin Aminiya ya ruwaito cewa hatsarin ya auku ne a kan babban titin Legas zuwa Ibadan, inda motar da yake ciki ta yi kaca-kaca.
kakakin Hukumar Kiyaye Haddura ta Kasa (FRSC) na Jihar Ogun, Afolabi Odunsi ya tabbatar da hatsarin da kuma mutuwar mutanen ga wakilinmu.
Ya ce, “Gaskiya ne, (Joshua) yana nan da ransa. Mutum biyar ne hatsarin ya rutsa da su, amma biyu su mutu. Zuwa anjima za mu fitar da sanarwa.”
Anthony Joshua wanda ke zaune a kasar Birtaniya dan asalin yankin Shagamu ne a Karamar Hukumar Shagamu ta Jihar Ogun
-
Opinion6 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion6 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News4 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
