News
Mutum 2 Sun Rasu Sakamakon Faɗawa Rijiya A Kano
Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da rasuwar mutane biyu bayan faɗawa rijiya a yankuna biyu dake jihar .
Mai magana da yawun hukumar, Saminu Yusuf Abdullahi, ya ce matashi mai shekaru 18, Yusif Malam Gwani Isah, ya faɗa wata rijiya a Kwanar Madugu, ƙaramar hukumar Ungogo. Hukumar ta aika da ƙungiyar ceto, amma matashin ya rasu kafin a kai shi asibiti.
Mutum 2 Sun Rasu Sakamakon Faɗawa Rijiya A Kano
A wani lamari daban, wani yaro mai shekaru 8, Abdussalam Ibrahim, ya faɗa rijiya a Kofar Yamma, ƙaramar hukumar Karaye. Ƙungiyar ceto ta isa wurin cikin gaggawa, amma yaron ya rasu.
Hukumar ta yi ta’aziyya ga iyalan mamatan sannan ta yi gargadi ga jama’a da su kula da yaran su.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
