News
Shugaba Tinubu Ya Tsige Sufeto Janar Na ‘Yan Sanda Kayode Egbetokun
Shugaban ƙasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya tsige Sufeto Janar na ‘Yan Sandan ƙasar, Kayode Egbetokun, daga mukaminsa, kamar yadda majiyoyi daga cikin manyan jami’an tsaro da kuma Police Service Commission suka tabbatar.
Rahotanni sun ce an umurci Egbetokun da ya shirya takardun miƙa mulki bayan wata ganawa da ya yi da shugaban ƙasa a fadar shugaban ƙasa, inda ake sa ran ya kammala mika ragamar aiki nan ba da jimawa ba.
Falalar Da Ke Tattare Da Azumin Watan Ramadan
A cewar majiyoyi, an naɗa Tunji Disu a matsayin sabon Sufeto Janar na ‘Yan Sanda. Kafin wannan naɗi, Disu shi ne Mataimakin Sufeto Janar mai kula da sashen binciken manyan laifuka na rundunar ‘yan sanda da ke Alagbon a Jihar Legas.
Wasu rahotanni sun ce an shawarci tsohon shugaban rundunar da ya sauka domin mayar da hankali kan lafiyarsa. Haka kuma, an ce wasu jami’an ‘yan sanda sun nuna goyon baya ga sauyin shugabancin.
Har zuwa yanzu, ba a fitar da cikakken bayani a hukumance kan dalilan sauyin ba, amma ana sa ran sabon shugaban rundunar zai fara aiki cikin gaggawa.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
