News
Kotu Ta Yankewa Wasu Alƙalai Hukuncin Watanni 36 A Gidan Yari
Kotu a Burkina Faso ta yankewa wasu manyan alƙalan kotun Majistare huɗu da jami’an hukumar fasa ƙwauri 3 hukuncin watanni 2 zuwa 36 a gidan yari sakamakon samunsu da cin hanci da rashawa.
Bayan gudanar da bincike na kwanaki da alƙali Jean Jacques Wend-Panga ya jagoranta, kotun ta samu alƙalan 4 da lafin karɓar cin hanci da rashawa tare da watsi da ƙarar da aka shigar kan jami’an na custom game da karɓar cin hanci, wannan yasa kotun yanke wa Alban Balanoe Some zaman gidan waƙafi na watanni 36 sai Mohamed Traore da Urbain Medah da Sandaogo Antoine Kabore da aka yankewa hukuncin zaman gidan yari na watanni biyu zuwa goma sha biyu tare da biyan tara tsakanin CFA miliyan biyu zuwa uku.
Gwamnatin Kano Ta Haramta Zuba Yashi Da Sauran Kayan Gini A Kan Titunan Jihar
A ɓangaren jami’an fasa ƙwaurin da suka haɗa da Oumarou da Jonas Yameogo da Zindi Nikiema kotu ta yanke musu zaman gidan yari na tawon watanni goma sha biyar da ƙarin watanni biyu na karɓar cin hanci.
A yayin sauraron ƙarar, alƙalin kotun ya ƙi amince wa da tuhumar masu laifin na garkuwa da azabtar da su a lokacin da suke tsare ana bincike.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
