Connect with us

News

Kotu Ta Yanke Wa Matasa Biyu Hukuncin Kisa Kan Kashe Ango A Kano

Published

on

kotu

Babbar Kotun Jihar Kano ta yanke wa wasu matasa biyu hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan ta same su da laifin kashe wani ango a wani hari na fashi da makami da suka kai cikin dare a Kano.

Wadanda aka yankewa hukuncin sun hada da Aliyu Hussaini da Amir Zakariyya, mazauna Sheka Sabuwar Abuja da Unguwar Malam a karamar hukumar Kumbotso. An same su da laifukan hada baki, fashi da makami da kuma kisan kai dangane da mutuwar Yazid Haruna.

Advertisement

Kotu Ta Yanke Wa Matasa Biyu Hukuncin Kisa A Kano

A hukuncin da ta yanke, Mai Shari’a Amina Adamu-Aliyu ta ce bangaren masu gabatar da kara sun tabbatar da tuhumar da ake yi wa wadanda ake zargin ba tare da wata shakka ba. Ta bayyana harin a matsayin mummuna kuma abin damuwa, musamman yadda ake samun karuwar hare-haren fashi da ke da alaka da satar wayoyin hannu a wasu sassan jihar.

Advertisement

Bisa bayanan masu gabatar da kara karkashin jagorancin Barrista Lamido Abba-Sorondinki, lamarin ya faru ne da misalin karfe 2:47 na daren ranar 11 ga watan Yunin 2025 a Sheka Sabuwar Abuja.

Kotun ta ji cewa wadanda aka yankewa hukuncin sun hada baki tare da daukar dogayen wukake da adda kafin su kai hari kan mamacin. A yayin harin, sun kwace wayoyi biyu da kuma Naira 19,500 daga hannunsa.

Advertisement

An kuma bayyana cewa sun soke shi sau da dama, lamarin da ya haddasa masa munanan raunuka da suka yi sanadin rasuwarsa daga bisani.

Masu gabatar da kara sun gabatar da shaidu uku tare da mika rahoton likita a gaban kotu domin tabbatar da zarge-zargen.

Advertisement

Sai dai wadanda ake tuhuma sun musanta laifukan. Lauyansu, Barrista Haruna Saleh-Zakariyya, ya roki kotu da ta yi la’akari da jin kai yayin yanke hukunci.

Kotun ta same su da laifi karkashin sashe na 97(1), 298(c) da 221(a) na Dokar Penal Code ta Jihar Kano.

Advertisement

An yanke wa kowannensu daurin shekara guda kan laifin hada baki, daurin rai da rai kan fashi da makami, sannan hukuncin kisa ta hanyar rataya kan laifin kisan kai.

A wani ci gaba mai alaka da wannan shari’a, an ruwaito cewa tun a ranar 20 ga Oktoban 2025 wata kotu a Kano ta riga ta yanke musu hukuncin kisa kan kisan wani malami a wani lamari daban da ya shafi fashi da wayar hannu.

Advertisement

 

DAILY TRUST 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending