News
Kotu Ta Yanke Wa Wanda Ya Kashe Mahaifinsa Hukuncin Daurin Rai Da Rai
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Wara Babbar kotu dake garin Minna ta yanke wa Abubakar Muhammad-Buba hukuncin daurin rai da rai bayan an kama shi da laifin kashe mahaifinsa.
Kotun ta gurfanar da Abubakar ranar 9 ga Oktoba 2023 bisa laifuka hudu da kisa, sata da sauran su.
Likitocin Asibitin Aminu Kano Sun Cire Min Mahaifa Da Jaririna Ba Tare Da Sanina —Maimunat
Rundunar ‘yan sandan dake Korokpa a kauyen Chanchaga ne suka kama Muhammad-Buba yayin da ya zo karban kudin filin mahaifinsa da ya siyar.
Bisa ga karan da aka shigar a kotun Muhammad-Buba ya caki mahaifinsa da wuka inda baya ya mutu ya yi gunduwa-gunduwa da shi ya zuba jikin a le da sannan ya jefar a kusa da madatsar ruwan Tagwai Dam dake Chanchaga.
Daga nan sai Muhammad-Buba ya je ya sanar da babban amincin mahaifinsa Kuma shugaban kungiyar masu hako na’adanai na jihar Naje Mohammed SD Mambo cewa an yi garkuwa da mahaifinsa Kuma nana bukatan wasu kudade na fansa.
Bayan ya karbi kudin fansan sai Muhammad-Buba ya kara sanar da abokin mahaifin cewa maharan da suka yi garkuwa da mahaifinsa sun sako shi amma mahaifin ya ji rauni kuma yana bukatan fida a asibitin Gwagwalada.
Daga baya dai Mambo ya gano cewa Muhammad-Buba karya yake masa inda hakan ya sa ya sanar da ‘yan sanda.
Alkalin kotun Mohammed S.A. Mohammed ya yanke wa Muhammad-Buba hukuncin daurin rai da saboda fannin da suka shigar da kara sun tabbatar wa kotun cewa shine ya kashe mahaifinsa.
Mohammed ya ce bisa ga laifin kisa da Muhammad-Buba ya aikata kamata ya yi a yanke masa hukuncin kisa amma ya yi masa sassauci ya yanke masa hukuncin daurin rai da rai.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
