News
Gwamnatin Kano Ta Nuna Damuwa Kan Karancin Komawar Dalibai Makarantu Bayan Kammala Hutun Sallah
Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana damuwa matuƙa kan yadda ɗalibai da dama ba su koma makarantu ba bayan kammala hutun Sallah ƙarama.
Babban Sakataren Ma’aikatar Ilimi ta jihar, Alhaji Bashir Baffa Muhammad, ne ya bayyana hakan a wata hira da kafar Arewa Radio, bayan da ya gudanar da rangadi domin duba halin komawar ɗalibai a wasu makarantun gwamnati.
Jami’an Hisbah Sun kama mata sama da 280 Da Su Ka Yi Shigar Banza A Bukukuwan Sallah A Kano
Ya ce ya ziyarci makarantu sama da 15 a faɗin jihar, inda ya tarar da ƙarancin halartar ɗalibai duk da cewa an buɗe makarantu a hukumance domin ci gaba da karatu.
A cewarsa, halin da aka tarar abin takaici ne, la’akari da yadda aka sanar da ranar komawa makaranta tun kafin ƙarshen hutun.
Gwamnatin ta yi gargaɗin cewa ba za ta lamunci ci gaba da irin wannan hali ba, tana mai cewa za ta ɗauki matakan da suka dace domin magance matsalar.
Haka kuma, ta yi kira ga iyaye da masu kula da yara da su tabbatar da cewa ‘ya’yansu sun koma makaranta cikin gaggawa, tare da jaddada muhimmancin ilimi ga ci gaban al’umma.
-
News5 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
-
News4 days ago
ICPC Ta Wanke Femi Gbajabiamila Daga Zargin Badakalar Hukumar Bogi
-
News5 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Dakile Yunkurin Sace Jariri Da Wasu Ma’aikatan Asibiti A Jigawa
