News
Amurka Ta Bai Wa Jami’anta Umarnin Barin Ofishin Jakadancinta Na Nijeriya
Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta bai wa ma’aikatanta da ba na gaggawa ba da iyalansu umarnin ficewa daga ofishin jakadancinta da ke Abuja, babban birnin Nijeriya saboda taɓarɓarewar tsaro a faɗin ƙasar.
A wasu jerin shawarwari da ta fitar ga Amurkawa ranar Laraba, ma’aikatar ta bayyana cewa, daga ranar 8 ga watan Afrilun shekarar 2026, an umarce su da su guji yin balaguro zuwa Nijeriya saboda yawaitar aikata laifuka da ta’addanci da garkuwa da mutane da kuma rashin zaman lafiya.
Jami’an Ƴansanda Sun Kama ‘Yan Ta’adda Da Ke Amfani Da Coci A Matsayin Maɓoya
Sanarwar ta ayyana gaɓa ɗaya balaguro zuwa Nijeriya a “mataki na 3: taka-tsantsan,” yayin da wasu jihohi suke a ”matakin 4: kada ku tafi.”
Ma’aikatar ta ƙara jihohin Filato da Jigawa da Kwara da Neja da Taraba cikin jerin wurare na “kada ka tafi,” lamarin da ya sa jumullar jihohin da aka matuƙar hana zuwa ta kai 23.
“Ranar 8 ga watan Afrilu na shekarar, ma’aikatar harkokin wajen ta bai wa ma’aikatan Amurka waɗanda ba na gaggawa ba damar barin ofishin jakadancin Amurka na Abuja saboda taɓarɓarewar lamarin tsaro,” in ji sanarwar.
“Ku sake tunani game da yin balaguro zuwa Nijeriya saboda laifuka da ta’addanci da rashin zaman lafiya da garkuwa da mutane da kuma rashin tabbacin samuwar kiwon lafiya. Wasu wurare suna da ƙarin hatsari,” in ji ta.
Mataki na 4 ya bayyana cewa an yi kira ga Amurkawa su ƙaurace wa jihohi na arewa da suka haɗa da Borno da Jigawa da Kogi da Kwara da Neja da Filato da Taraba da Yobe da kuma arewacin jihar Adamawa saboda ta’addanci da laifuka da garkuwa da mutane.
Kazalika shawarar ta lissafa jihohin Bauchi da Gombe da Kaduna da Kano da Katsina da Sokoto da kuma Zamfara inda ta yi ishara da rashin zaman lafiya da aikata laifuka da garkuwa da mutane.
