Connect with us

News

Amurka Da Iran Sun Gaza Cim Ma Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Tattaunawarsu Ta Pakistan

Published

on

5a2a6960 9bc7 4226 954b 1897b5d19e7b.jpg

Mataimakin Shugaban Amurka JD Vance ya bayyana cewa tattaunawar da aka yi da Iran ta gaza cim ma matsaya, yana mai ƙari da cewa Amurka ta gabatar da “buƙata ta ƙarshe kuma mafi kyawu” bayan doguwar tattaunawa da aka yi a birnin Islamabad na Pakistan.

Da yake magana bayan shafe kusan sa’o’i 21 ana tattaunawa a babban birnin Pakistan, Vance ya ce har yanzu Amurka tana bai wa Iran lokaci don ta yi la’akari da buƙatun da aka gabatar.

Advertisement

HARIN DAKARUN SOJIN SAMA: Mun Rufe Kasuwar Jilli Shekaru 5 Da Suka Wuce — Gwamnan  Borno

“Mun bar nan da tabbatacciyar buƙata, wata hanyar fahimta wadda ita ce tayinmu na ƙarshe kuma mafi kyawu. Za mu gani ko Iraniyawa za su karɓa,” in ji shi.

Advertisement

Vance ya ce tawagar Iran ta zaɓi rashin karɓar sharuɗɗan Amurka, inda ya ƙara da cewa tattaunawar ba ta riga ta samar da sakamako mai gamsarwa ba.

“Ba mu ga hakan ba tukuna. Muna fatan za mu gani,” in ji shi, yana nufin alƙawari daga Iran na tabbatar da daina ƙera makaman nukiliya.

Advertisement

Ya bayyana cewa babban abin da ke haddasa taƙaddamar shi ne shirin nukiliyar Iran, yana mai jaddada cewa Amurka tana neman tabbaci na dogon lokaci.

“Gaskiyar magana ita ce, muna buƙatar ganin tabbataccen alƙawari cewa ba za su yi makamin nukiliya ba, kuma ba za su nemi kayan aikin da za su ba su damar ƙera makamin cikin sauri ba,” in ji Vance.

Advertisement

 

Iran ta yi watsi da buƙatu masu ‘yawa

Advertisement

Iran ta bayyana cewa tattaunawar za ta yi nasara ne kawai idan Amurka ta janye abin da ta kira buƙatu masu “yawa” waɗanda suka “saɓa wa doka.”

Kakakin Ma’aikatar Wajen Iran, Esmaeil Baghaei, ya ce ci gaban tattaunawar ya dogara ne kan yadda Amurka za ta nuna “gaskiya da niyya mai kyau” sannan ta amince da “haƙƙoƙi da muradun Iran na halal.”

Advertisement

“Nasarar wannan tsari na diflomasiyya ta dogara ne kan gaskiya da niyya mai kyau na ɓangaren da muke adawa da shi, da guje wa buƙatu masu yawa da waɗanda suka saɓa wa doka, da kuma amincewa da haƙƙoƙi da muradun Iran na halal,” in ji shi.

Baghaei ya ƙara da cewa tattaunawar ta ci gaba ba tare da tsayawa ba, inda aka yi musayar saƙonni da rubutattun buƙatu tsakanin ɓangarorin biyu.

Advertisement

Ya ce tattaunawar ta shafi batun Mashigar Hormuz, shirin nukiliyar Iran, biyan diyyar yaƙi, ɗage takunkumai, da kuma “kawo ƙarshen yaƙi baki ɗaya a kan Iran da ma yankin baki ɗaya.”

Haka kuma, Baghaei ya ce Iran ba ta manta da abin da ya kira “yaudarar” Amurka da kuma tarihin saɓa alƙawuran da ta yi a baya ba.

Advertisement

 

TRT AFRIKA 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending