Connect with us

News

Siyasa Ce Ta Fi Dacewa Da Malamai Ba Kamasho Ba —Malam Ibrahim Khalil

Published

on

122493390 ibrahim khalil.jpg
Sheikh Ibrahim Khalil, fittacen malamin addinin Musulunci kuma shugaban majalisar malamai a Kano

Sheikh Ibrahim Khalil, fittacen malamin addinin Musulunci kuma shugaban majalisar malamai a Kano, ya bayyana cewa ya fi dacewa malamai su shiga harkokin siyasa maimakon ci gaba da zama cikin abin da ya kira “kamasho” a halin yanzu.

Malamin ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da ya yi da Matashiya TV, inda ya jaddada cewa tun tarihi malamai su ne suka kasance a matsayin shugabannin al’umma.

Advertisement

Jami’an ‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Kaduna

A cewarsa, kasancewar malamai suna da ilimi da fahimtar al’amuran rayuwa, ya kamata su taka rawar gani a siyasa domin ba da gudunmawa wajen inganta shugabanci.

Advertisement

“Bai dace malamai su zama ‘yan kamasho kamar yadda ake gani a yanzu ba. Siyasa ita ce hanya mafi dacewa da za su bi domin kawo gyara a al’umma,” in ji shi.

Ya kuma kara da cewa shigar malamai cikin siyasa na iya taimakawa wajen samar da shugabanci nagari da kuma ci gaban kasa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending