Connect with us

News

MNJTF sun hallaka ƴan ta’adda 300 a arangama 30 da suka yi a tafkin Chadi

Published

on

Daga Maryam Bashir Musa 

 

 

 

Rundunar haɗin gwiwa ta Multinational Joint Task Force, MNJTF, a jiya Asabar ta ce ta hallakamayakan Boko Haram da ISWAP 300, a yankin Arewa-maso-Gabas a tafkin Chadi.

Kamarudeen Adegoke, babban jami’in yada labarai na rundunar soji ta MNJTF N’Djamena, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Maiduguri, ya ce an kashe ƴan ta’addar ne a arangama 30 daban-daban.

Advertisement

Adegoke, wanda ya ke da muƙamin Laftanar-Kanar, ya bayyana cewa, Kwamandan rundunar, Abdul Khalifa, ya bayyana haka a lokacin wani taro da daukacin kwamandojin MNJTF da aka zaɓo daga kowane bangare.

Khalifa ya ce an shirya taron ne domin yin nazari a ayyukan da aka riga a ka gudanar a halin yanzu domin shirye-shiryen tunkarar aiki na gaba.

A cewarsa, sama da ‘yan ta’adda 52,000 da suka hada da mayaka, wadanda aka maida su ƴan ta’adda ta karfi da yaji da kuma iyalansu sun mika wuya a yankunan da MNJTF da Op Hadin Kai da ke gudanar da ayyukansu.

Ya kuma yi kira ga ƴan ta’addan, da su ƴan Boko Haram ne ko kuma ISWAP ne, da su yi fita da ga wannan kungiyar ta masu aikata laifuka su kuma mika wuya kamar yadda dubban ƴan uwansu suka yi kafin lokaci ya ƙure musu.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending