News
Rukunin gidaje na ‘Buhari Estate’ na ‘yan sanda ne ba ‘yan bindiga ba – ‘Yan sandan Najeriya
Daga maryam bashir musa
Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta musanta rahotannin da ke cewa ‘yan bindiga sun mamaye wani rukunin gidaje mai suna Buhari Estate da ta mallaka a yankin Badagry na Jihar Legas.
Tsohon Ministan Harkokin Ƙasashen Waje ya samu tikitin takarar Sanatan Jigawa a PDP
Cikin sanawar da fitar a yau Asabar, rundunar ta ce wani mutum ne “da ya yi kama da mai ilimi wanda ya kamata a ce ya san haɗarin yaɗa labaran ƙarya yake yaɗa bayanai da zimmar tayar da fitina” a wani bidiyo, yana iƙirarin cewa ‘yan bindiga ne suka mamaye rukunin gidajen.
Sanarwar ta ce rukunin gidajen mallakin rundunar ne kuma jami’an ‘yan sanda ne da iyalansu suka mallake su ta hanyar wani shirinta.
“Rundunar ‘yan sanda na shawartar mutane kan muhimmancin tantance abu kafin yaɗa shi don kauce wa tashin hankali, musamman idan aka yi la’akari da mabambantan ƙabilun da ke cikin ƙasa [Najeriya],” in ji rundunar.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
