News
Ganduje ya sake naɗa Baffa Dan’agundi a matsayin shugaban CPC na riƙo
Daga Kabiru basiru fulatan
Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya amince da naɗin Shugaban Hukumar kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Kano, KAROTA, Baffa Babba Dan’agundi a matsayin Shugaban Hukumar Kare Hakkin mai Saye, CPC na riƙo.
Hajjin bana: An kai raguna 50,000 daga Afirka zuwa Saudiya domin yin hadaya
Daily Nigerian Hausa ta tuna cewa Ganduje, a shekarar da ta gabata ya naɗa Dan’agundi a matsayin shugaban CPC din na riƙon ƙwarya kafin ya naɗa Idris Dambazau a matsayin shugaban hukumar na din-din-din.
A wannan karon ma, a wata sanarwa da Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamna Ganduje, Abba Anwar ya fitar a yau.
Sanarwar ta ce naɗin na Dan’agundi ya fara aiki ne nan take, inda ya ce kuma an bashi damar kula da dukkanin al’amuran hukumar har zuwa lokacin da za’a naɗa Manajan Daraktar hukumar na din-din-din.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
