News
Hatsarin mota ya kashe mutum 18 a kan titin Legas zuwa Ibadan
Daga kabiru basiru fulatan
Mutum aƙalla 18 ne suka rasa rayukansu sakamakon hatsarin mota da ya afku a kan babbar hanyar Legas zuwa Ibadan na Jihar Oyo da ke kudancin Najeriya, kamar yadda hukumomi suka bayyana ranar Lahadi.
Peter Obi ya gargaɗi magoya bayansa kan maja da Kwankwaso
Mai magana da yauwn hukumar kiyaye haɗura ta ƙasa a Najeriya, Bisi Kazeem, ya ce lamarin ya faru da misalin ƙarfe 10:20 na dare a ranar Asabar a kusa da Gadar Isara, inda hatsarin ya ritsa da mutum 25.
Mista Kazeem ya ƙara da cewa gudun wuce kima da kuma karya ƙa’idojin tuƙi ne suka haddasa hatsarin da ya jawo mutuwar mutanen.
Mutum shida daga cikin 25 ɗin maza ne, da mace ɗaya, sai kuma yaro namiji ɗaya. Sai dai kuma ba a iya tantance sauran mutum 17 ba.
Karo da motocin suka yi ya haifar da fashewa da tashin gobara, inda ya ƙunshi motoci uku, a cewar sanarwar da Mista Kazeem ya saka wa hannu.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
