News
An kama Wani fursuna da ya tsere a kurkukun kuje
Daga yasir sani Abdullahi
Rundunar Yan SANDAN jahar katsina da ke arewacin Nigeria ta ce Jami,anta sunyi nasarar kama Wani fursuna Daya da ya tsere daga kurkukun kuje da ke Abuja babban birnin tarayya kasar
A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Gambo Isah, ya fitar
A jiya juma,a’ ya ce an kama fursunan ne mai suna Kamala Abubakar a wani samame da aka kai a maboyar bata-gari a jihar.
‘Yan bindiga sun kai hari kan gidan-yarin na Kuje ne a ranar 5 ga watan Yuli , inda aka tabbatar da cewa fursunoni 879 ne suka tsere, cikin su kuwa har da wadan da ake zargi Yan Boko Haram ne
Sai dai fursunoni da dama sun koma don radin kansu amma kawo yanzu ana neman fursunoni 443.
Tun bayan faruwar lamarin, an yi nasarar sake kamo kadan daga cikin fursunonin a wasu sassan kasar, da suka hada da jihar Ogun da Nasarawa.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
