News
Buhari ya ba ministan ilimin Najeriya umarnin kawo ƙarshen yajin aikin ASUU cikin mako biyu
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayar da umarni ga ministan ilimi na ƙasar Malam Adamu Adamu da ya kawo ƙarshen yajin aikin malaman jami’o’in ƙasar.
Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito cewa shugaban ya bayyana haka ne a ranar Talata inda ya bayar da umarni ga ministan ilimin ƙasar da ya sasanta abubuwan da ake taƙaddama a kai cikin mako biyu sa’annan a kai masa rahoto.
Kotu Ta Janye Umarnin Hana Ganduje Karbo Bashin N10bn
A yau Talata Shugaba Buharin ya tattauna da ma’aikatu da masu ruwa da tsaki waɗanda ke da alaƙa da ɓangaren ilimi a ƙasar da za su iya warware wannan tirka-tirkar.
Shugaban ya kira su ne domin ya samu ƙarin bayani kan dalilin da ya sa wannan yajin aikin ya ƙi ci ya ƙi cinyewa.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
