News
Mun fi samun tsaro lokacin Jonathan — Ƙungiyar ƴan Arewa By muhammad muhammad zahraddin December 30, 2021 0
Gamaiyar Ƙungiyoyi masu Zaman Kansu a Arewa, a ƙarƙashin inuwar CNG, sun koka kan yawaitar garkuwa da mutane, kashe-kashe da rashin tsaro a ƙasar nan.
Daraktan sadarwa na CNG, Ismail Musa ya ce Shugaba Muhammadu Buhari ya dawo da Nijeriya kamar lokacin tsohon shugaban ƙasa Jonathan Goodluck, lokacin da rashin tsaron bai yi ƙamari ba kamar yanzu.
A wani shirin tattaunawa na jaridar Vanguard a jiya Laraba, Musa ya caccaki Buhari kan yadda ya gaza daƙile rashin tsaro a ƙasa.
“Mu yanzu abin da mu ke roƙon su shine, ka san rayuwar ɗan adam na da daraja, ita ce ma ƙashin baya.
“Mu in ma za ka yi wani abu, to ka maida mu baya lokacin da ka samu yanayin rashin tsaro, ka ga za mu iya cewa mun hakura da hakan saboda kamar yadda kididdiga ta nuna, kowa ya san dai ba kamar yanzu ba.
“To gaskiya, mun shiga uku a ce irin waɗannan mutanen ne su ke mulkar mu,” in ji shi.
Advertisements
-
News5 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News3 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
-
News5 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
