News
2023: APC ta sulhunta Goje da gwamnan Gombe, Y
Daga kabiru basiru fulatan
Kwamitin Shugabacin Jam’iyar APC na Wucin-gadi, ƙarƙashin jagorancin Mai Mala Buni ya sulhunta tsakanin Gwamna Muhammad Yahaya na Jihar Gombe da kuma abokin burmin sa na siyasa, tsohon gwamnan jihar, Sanata Ɗanjuma Goje.
Jami’in Yaɗa Labarai na Buni, Mamman Mohammed ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a jiya Laraba a Abuja.
Ya ce Buni, da Shugaban Kwamitin Sulhu na APC, Sanata Abdullahi Adamu da Kashim Shattima, mamba a kwamitin, su su ka jagoranci sulhun.
Sanarwar ta ce wannan shine karon farko da manyan ƴan siyasar na Gombe su ka haɗu tun bayan da rigimar siyasa ta ɓarke tsakanin su a shekarar bara.
Buni, wanda shine kuma Gwamnan Jihar Yobe, ya baiyana jin daɗin sa game da sulhun da a ka yi.
Ya kuma ci alwashin sulhunta duk masu ruwa da tsaki a APC domin ƙarfafa jam’iyar yayin da a ke tunkarar kakar zaɓe ta 2023.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
