Sports
Najeriya ta fi ko wacce kasa ƙoƙari a gasar Afcon – CAF
Daga muhammad muhammad zahraddin
Hukumar kwallon kafa ta Afrika CAF ta ce Najeriya ce kasar da ta fi ko wacce kasa kokari a gasar cin kofin kasashen nahiyar Afrika da ake gudanarwa a Kamaru.
Wannan ya biyo bayan maki 9 da kasar ta hada a duka wasanninta da ta ci na rukuni, inda CAF a wani sakon Twitter da ta wallafa ta ce rabon da a nuna irin wannan bajinta tun 2010, lokacin da kasar Masar ta yi.
Yanzu dai Najeriya za ta hadu da kasar Tinusia a wasan gaba da za a fara bugawa a ranar Lahadi. A wani sakon na daban CAF ta wallafa cewa kocin Najeriya Augustine Eguavoen shi ne kocin da ya fi ko wanne kwarewa ya zuwa yanzua gasar.
-
News6 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News3 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
-
News6 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
