Connect with us

News

Majalisa Ta Yi Watsi Da Kudurin Hana Jami’an Gwamnati Tura ‘Ya’yansu Karatu Waje.

Published

on

FB IMG 1646371214657
Spread the love

Daga yasir sani abdullahi

 

 

Advertisement

Yan majalisar wakilai a ranar Alhamis, 3 ga watan Maris, sun yi watsi da kudirin dokar da ke neman hana jami’an gwamnati tura ‘ya’yansu makaranta zuwa kasashen ketare.

Wasu daga cikinsu sun dage kan cewa hakan ya saba wa muhimman hakkokin ‘yan Najeriya.

Kudirin dokar na Sergius Ogun, ya nemi a tabbatar da cewa jami’an gwamnatin da za su iya nuna cewa za su iya daukar nauyin ‘ya’yansu a kasashen waje ba tare da amfani da kudin gwamnati ba ne kadai za su iya hakan.

Advertisement

‘Yan majalisar sun roki Mista Ogun da ya janye kudirin amma ya ki, kuma da aka kada kuri’a, sai akasarin kuri’un suka nuna kin amincewa da kudirin.

Daga karshe, kudurin da ke neman sauya sashe na 46 a kundin kiwon lafiya ya sha kaye a majalisa bayan dogon caccaka tsinke daga nan aka yi watsi da shi.

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *