News
Ba zan yadda na zama mataimakin ɗan takara ga kowa ba — Kwankwaso
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Ɗan takarar shugabancin kasa a jam’iyyar NNPP, Rabi’u Musa Kwankwaso ya ce ba zai amince ya zama mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa ba ga kowa ba.
Daraktan Shirin Izzar So Ya Rasu
Kwankwaso, tsohon Gwamnan Jihar Kano, ya ce amincewa da zama mataimakin duk wani dan takarar shugaban kasa zai haifar da rugujewar jam’iyyar NNPP mai kayan marmari.
Kwankwaso, wanda ya je Jihar Gombe domin ƙaddamar da ofishin jam’iyyar NNPP na jihar da kuma ganawa da Zaɓaɓɓun ƴaƴanjam’iyyar a jiya Asabar, ya bayyana haka a wata hira da manema labarai.
Ya ce martabar siyasarsa da aka gina tsawon shekaru da kuma ɗimbin gogewarsa ta aiki da muƙamai daban-daban da ya riƙe a ƙasar nan ya taimaka wajen ganin jam’iyyar NNPP ta yi suna cikin ƙanƙanin lokaci.
Ya bayyana cewa da irin ɗaukakar da jam’iyyar NNPP ta samu cikin ƙanƙanin lokaci, duk abin da ya gaza shugabancinsa a karkashin jam’iyyar zai haifar da rugujewar jam’iyyar NNPP.
Kwankwaso ya tabbatar da cewa jam’iyyarsa ta dade tana tattaunawa da jam’iyyar Labour domin yiwuwar haɗewa, inda ya ƙara da cewa babban abin da ya hana samun ci gaba shi ne batun wanda zai zama ɗan takarar shugaban ƙasa.
-
Opinion7 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion7 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News5 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
