News
Yan Bindiga Sun Harbe Mataimakin Kwamishinan ’Yan Sanda A Katsina
Daga kabiru basiru fulatan
’Yan bindiga sun harbe wani Mataimakin Kwamishinan ’Yan sanda, Aminu Umar a Jihar Katsina.
Bayanai sun ce an ’yan bindigar sun yi wa mataimakin kwamishinan ’yan sandan da tawagarsa kwanton bauna ne a lokacin da suke sintiri a dajin Zakka da ke Karamar Hukumar Safana ta jihar.
Wakilinmu ya ruwaito cewa, gabanin rasuwarsa, Aminu Umar shi ne kwamandan rundunar ’yan sanda na yankin Dutsinma.
Majiyoyi a yankin na Zakka sun shaida wa Aminiya cewa, ’yan sanda da ’yan bindiga sun yi arangamar ce a wani kauye mai suna Yauni da ke gundumar Zakka a cikin garin Safana.
Da yake tsokaci kan lamarin, jami’in hulda da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Katsina, SP Gambo Isah, ya ce Umar ya mutu ne a karon-battar da ’yan sanda suka yi da ’yan bindiga sama da 300.
Ya ce akwai kuma karin wani ya riga mu gidan gaskiya a sakamakon artabun, sai dai bai bayyana ko wane ne dayan da ajali ya katse wa hanzari ba.
Source Aminiya
-
News2 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News7 days ago
2027: INEC Ta Tabbatar Da Ibrahim Ali Amin Little A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano A Jam’iyyar ADC
-
News5 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
