News
Matashiyar da ke bayar da hayar kayan biki a Kano
Daga Maryam bashir musa
Wata matashiya a jihar Kano da ke arewacin Najeriya ta bude shagon bayar da hayar kayan biki da mata ke sanyawa a lokutan bukukwansu.
BBC Hausa ta rawaito Habiba Yusha’u wacce akafi sani da Beebas Glam, ta ce ta fara sana’ar ce bayan fahimtar yadda mata ke kashe kudi wajen sayan kayan tufafi yayin bikinsu wanda kuma ba su bukatar shi bayan bikin.
Guguwa ta lalata gidaje da gine-gine 1,300 a Jigawa
“Idan akayi lakari a kasar Hausa kusan duk bikin da za a yi, za ka ga amarya ta saka tufafi wanda sau daya kawai ake daura shi domin idan ta saka shi bayan biki za’a rika mata kallon mahaukaciya”.
Habiba tsohuwar mai sana’ar kwalliya ce amma a yanzu tafi mayar da hankali ne wajen bayar da hayar kayan amare lokacin bikinsu.
Matashiyar ta ce akwai duk irin kayan da amarya ke bukata kuma cikin farashi mai sauki saboda ta fara sana’ar ce domin taimakawa talakawa da marayu tun da ita ma marainiya ce.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
