Connect with us

News

Sabuwar Shekarar Musulunci: Ganduje Ya Ayyana Litinin A Matsayin Ranar Hutu A Kano

Published

on

Ganduje

 

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Gwamnatin Jihar Kano ta ayyana ranar Litinin, daya ga watan Agustan 2022 a matsayin ranar hutu don murnar shiga sabuwar shekarar Musulunci ta 1445.

Advertisement

 

Kwamishinan Yada Labarai na Jihar, Muhammad Garba ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwar da ya fitar da maraicen Laraba a Kano.

Advertisement

 

CBN ta baiwa TajBank lasisin gudanar da harkoki a faɗin ƙasa

Advertisement

Ya ce Gwamnan Jihar, Abdullahi Umar Ganduje, ya taya daukacin al’ummar Musulmin jihar murna zagayowar shekarar mai cike da albarka.

 

Advertisement

Ya kuma yi kira gare su da su yi amfani da lokacin wajen neman yafiyar Ubangiji musamman kan kalubalen tsaron da kasar nan ke fama da shi.

 

Advertisement

Sanarwar ta kuma ce Gwamnan ya yi kira ga duk wadanda ba su mallaki katin zabensu ba da su gaggauta yin hakan don samu su kada kuri’arsu a zaben 2023 da ke tafe.

 

Advertisement

Sabuwar shekarar Musuluncin ta bana dai, wacce za ta fara a farkon watan Almuharram, za ta shiga ne ranar Asabar, 30 ga watan Yulin 2022

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending