Connect with us

News

A bi a hankali wajen neman tsige Buhari, In ji Kwankwaso

Published

on

Kwankwaso

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Ɗan takarar shugaban ƙasa a inuwar jam’iyyar NNPP a Najeriya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ja hankalin wasu daga cikin ‘yan majalisa kan su bi a hankali wajen neman tsige shugaba, Muhammadu Buhari.

Advertisement

Dalilin Da Ya Sa Ba Za Mu Kara Wa’adin Yin Rajistar Zabe Ba — INEC

Jaridar Daily Trust ta Najeriya ta rawaito cewa Kwanwaso ya faɗi hakan ne a Ilorin a ziyarar da ya kai wa gwamna ABdulRahman AbdulRazaq.

Advertisement

Sanata Kwankwaso na cewa kada ‘yan majalisa su yi gaggawa wajen aiwatar da matakinsu.

Ɗan takarar ya ce babu shaka akwai damuwa matuƙa kan halin da tsaron ƙasa ke ciki tare da shawarta gwamnati ta dau wannan a matsayin babban kalubale a gareta.

Advertisement

Kwankwaso, wanda tsohon ministan tsaro ne, ya roƙi gwamnati ta yi harama wajen sauraren koken al’umma da shawo kan matsalolin da suka addabesu.

Kwankwaso na wannan ziyarar ne a Ilorin domin bude sabuwar ofishin NNPP da kuma na sauran jihohi makwabta.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending