News
Dalilin Da Ya Sa Ba Za Mu Kara Wa’adin Yin Rajistar Zabe Ba — INEC
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta ce da zarar wa’adin da ta sa na ranar 31 ga watan Yulin 2022 domin kammala rajistar masu zabe ya cika, ko kwana daya ba za ta sake karawa ba.
Kwamishinan Hukumar mai kula da bangaren wayar da kan masu zabe, Festus Okoye ne ya bayyana hakan a Awka, babban birnin jihar Anambra, yayin zantawarsa da ’yan jarida a ranar Asabar.
Newcastle za ta raba Werner da Chelsea, Azpilicueta da Alonso za su koma Barcelona Timo Werner
Ya ce za a rufe yin rajistar ce domin hukumar ta sami damar ci gaba da sauran shirye-shiryen babban zaben 2023 da ke tafe.
A cewar Festus, da zarar wa’adin ya cika, hukumar za ta fara aikin tantance rajistar domin gano wadanda suka yi fiye da sau daya da kuma aikin buga katinan zaben.
Kwamishinan ya kuma ce wadanda suka yi rajistar da kuma wadanda suka sabunta ta daga tsakanin watan Janairu zuwan Yunin 2022, za su karbi katinansu a watan Oktoba mai zuwa.
Sai dai ya ce mutanen da suka yi rajistar a watan Yuli kuwa za su jira sai a watan Nuwamba mai zuwa kafin su fara karbar katinan nasu.
Da yake amsa tambaya a kan irin shirin da INEC ta yi wa zaben na 2023 kuwa, Festus Okoye ya ce a shirye suke su gudanar da sahihi kuma ingantaccen zabe da jama’a za su amince da shi.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
