Connect with us

News

NNPP za ta ƙwace mulki a hannun Zulum a zaɓen 2023, In ji Kwankwaso

Published

on

Kwankwaso

Daga: Muhammad Muhammad zahraddin

Ɗan takarar shugabancin kasa a inuwar sabuwar jam’iyya ta hamayya, NNPP, Rabi’u Musa Kwankwaso ya ce jam’iyyarsa za ta kwace mulki daga hannun gwamna Babagana Umara Zulum a zaɓen 2023.

Advertisement

Kwankwaso ya shaida hakan ne a birnin Maiduguri lokacin bude ofishinsu na kamfen a ranar Asabar.

Sanata Kwankwaso ya ce jam’iyyarsa ce za ta lashe zaɓe a Najeriya tun daga matakin jihohi har Tarayya.

Advertisement

Sannan ya buƙaci magoya bayansa su kasa su kuma tsare kamar yada ya aiwatar a Kano a lokutan zaɓe.

Kwankwaso ya je Maiduguri ne kwana biyu bayan hukumar raya birane ta jihar ta rufe ofishinsu kafin daga bisani gwamna Zulum ya umarci a sake buɗe ofishin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending