News
Saudia ta cire cire shingen hana taɓa jikin Ka’abah
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hukumomin Saudiyya sun cire shingen da suka sanya don hana alhazai tabawa da kuma sumbatar Al-Hajar Al-Aswad da kuma Kaʿabah.
An cire kariyar ne wadda ta kewaye Ka’abah wadda aka sa a lokacin annobar korona domin hana mutane, yayin da aka fara aikin Umrah.
Ana ta yada hotunan masu ibadah da suke ta kokarin taba Al-Hajar Al-Aswad din.
Sarki Salman ya isa Makkah don kammala azumin watan Ramadan
A farkon shekarar nan hukumomin kasar ta Saudi Arabia suka janye yawancin matakan kariyar da suka sanya na kokarin dakile annobar korona.
Aikin Hajjin da aka kammala a watan da ya gabata ya kasance kusan yadda ake yi a shekarun baya kafin daukar matakan kariya na korona, bayan shekara biyu da ta tsauraran matakai da aka dauka na rage yawan mahajjata.
-
Opinion3 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion3 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News3 days ago
Jihar Kano Ta Shiga Jerin Jahohi 10 Mafi Tara Kudaden Shiga Na VAT A 2026
