News
Mutane da dama suna cigaba da rasa muhallinsu na zama a Nguru
Daga Idriss Hussain Nguru
Al, umma na cigaba da rasa muhallinsu na zama sakamakon ambaliyar ruwan sama da aka samu a yankin unguwar barma lamarin Ya zama barazana ga Al, ummar karshen kwalta
jaridar INDARANKA ta rawaito cewa har Zuwa wannan lokacin ba, asan adadin mutanan da abun Ya shafa ba, Ansamu asarar dukiyoyi da dama.

Yau tsawon sati uku kenan da al’umar
yankin suka fara barin gidajensu, haka zalika a halin yanzu wasu daga cikinsu sun samu gidajen aro, wasu Kuma na haya, wasu ko har yanzu basu ga tsuntsu basu ga tarko.

kawo yanzu babu wani agaji da suka samu a hukumance. Kuma har izuwa yanzu kullum gidajen rushewa suke daga gidajen kasa (laka) har da na zamani saboda ruwan yaci karfinsu.

Muna kara kira ga hukumomi da su taimaka wajan fitar da wannan ruwa zuwa inda ya dace domin barnar da yakeyi bazata misaltuba.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
