News
Ƙungiyar ASUU za ta ɗaukaka ƙarar hukuncin da kotu ta yanke na ta janye yajin aiki
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADEEN
Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya ASUU ta shirya daukaka kara kan umarnin da kotun masana’antu ta bata na dakatar da yajin aikin da ta kwashe watanni Bakwai tana yi.
A wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar shiyyar Lagos, Mr Adelaja Odukoya, yace kungiyar ta bukaci Yayanta da su kwantar da hankalinsu akan umarnin Kotun Kuma su jira mataki na gaba
Sanatoci sun yi shiru kan tsige Buhari
Kungiyar ta ce tuni lauyanta ya shigar da kara akokarin bin kadin wannan umarni.
Sanarwar tace; “Ku kwantar da hankalinku.” Ta kuma bukaci mambobin kungiyar da ‘yan Najeriya da su kasance masu hadin kai, duk da cewa za a janye wannan umarni.
Sanarwar ta kara da cewa; “Shugaban kungiyarmu, Kwamared Victor Osodeke, ya bukaci mambobin kungiyarmu ta kasa da su kwantar da hankalinsu domin babu wani abin damuwa a bayan aiki da aka gabatar a yau.
“Lauyan mu ya shigar da kara dan dakatar da aiwatar da wannan hukuncin. Ba za a taɓa yin galaba a kan jama’ar da ke haɗin kai ba tare da sulhu ba.
-
News2 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News5 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
-
News5 days ago
Kwamitin Tsara Kundin Yakin Neman Zaɓen Gwamnan Kano Ya Yi Taron Tsare-tsare Manufofin Ci Gaban Jihar A Kaduna
