Connect with us

Sports

Man City ta yi wa Man United luguden kwallaye a Premier

Published

on

Yan wasa

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

Manchester City ta doke Manchester United da ci 6-3 a wasan makon na takwas a gasar Premier League da suka kara ranar Lahadi a Etihad.

Tun kan hutu City ta ci kwallo 4-0 ta hannun Phil Foden da Erling Haaland kowanne ya ci bibiyu.

Gwamnatin kano ta Samar da sabon asibitin idanu

Bayan da suka huta suka koma karawar zagaye na biyu Foden da Haaland kowanne ya kara zura kwallo a raga.

Sai dai United ta zare uku ta hannun Dos Santos, sannan Anthony Martial ya zura biyu a raga daya daga ciki a bugun fenariti.

Advertisement

Da wannan sakamakon City tana mataki na biyu a kan teburin Premier da maki 20, United kuwa tana nan da makinta 12 tana ta shida a teburin wasannin bana.

Manchester City ta yi nasara karo uku a jere a kan United tun bayan doke ta hudu da ta yi tsakanin Afirilun 2013 zuwa Nuwambar 2014.

United ta yi rashin nasara karo na 18 a Premier League a hannun City, – Liverpool da Chelsea sun yi nasara a kan United irin haka a babbar gasar tamaula ta Ingila.

Wasan da suka fafata a bara:

2021/2022

Premier League Lahadi 6 ga watan Maris 2022

Advertisement
  • Man City         4 – 1     Man Utd

Premier League 6 ga watan Nuwamba 2021

  • Man Utd          0 – 2     Man City

 

 

 

BBC

 

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending