News
An Sako Ragowar Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADEEN
’Yan bindiga sun sako fasinjoji 23 da suka rage a hannunsu daga cikin mutanen da suka yi garkuwa da su a Jirgin Kasan Abuja-Kaduna.
An Kashe Malamai 10, An Sace 50 A Wata 10 A Kaduna
Hedikwatar Tsaro ta Najeriya ta tabbatar cewa a ranar Laraba da La’asar ne aka mika fasinjojin su 23 ga Kwamitin Shugaban Kasa da Babban Hafsan Tsaro, Janar Lucky Irabor, ya kafa.
A ranar 28 ga watan Maris, 2022 ne ’yan ta’addan Boko Haram suka kai harin bom kan jirgin kasan da ke hanyarsa ta zuwa Kaduna daga Abuja inda suka kashe akalla mutum tara, suka yi awon gaba da wasu kimanin 60.
DAILY TRUST
Advertisements
