News
Mahaifin ɗan sandan da abokin aikinsa ‘ya kashe’ shi a Kebbi yana so a bi masa hakkinsa
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Mahaifin ɗan sandan nan da ake zargin abokin aikinsa ya kashe shi a jihar Kebbi da ke Najeriya sanadiyyar saɓani tsakaninsu, ya nemi hukumomin ƙasar su bi wa iyalinsa hakki.
Sani Shua’aibu Malumfashi, a tattaunawarsa da BBC kan kisan ɗan nasa ya ce a shirye yake ya bi kadin lamarin har sai an yi wa iyalan nasa adalci.
Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar ta Kebbi dai ya tabbatar wa BBC cewa tuni aka kai batun kisan na ASP Shu’aibu Sani sashen binciken manyan laifuka na rundunar da ke Kebbi, domin gano gaskiyar abin da ya faru.
Advertisements
