News
Kotun Ɗaukaka Ƙara ta ce DSS ta ci gaba da riƙe Nnamdi Kanu
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja a Najeriya ta tabbatar da buƙatar da gwamnatin tarayya ta shigar ta neman hukumar tsaro ta farin kaya ta ci gaba da riƙe jagoran masu fafutukar kafa ƙasar Biafra, Nnamdi Kanu.
Hakan na nufin kotun ta sauya hukuncinta na farko na cewa a saki Kanu.
DSS ta musanta kai samame wani gida a Abuja tare da sojojin Amurka
Gwamnatin Najeriya ta ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Ƙoli ne bayan da Kotun Daukaka Kara a ranar 13 ga watan Oktoba ta ba da umarnin sakin Kanu.
Advertisements
